Wed. Apr 2nd, 2025

Ana Cigaba Da Alhinin Rasuwar Fitaccen Ɗan Siyasa Ahmad Haruna Zango

By Saleh Aliyu Feb 13, 2025

Daga Ibrahim Muhammad

Fitaccen ɗan siyasa a jihar Kano, kuma shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta Jihar, Ambasada Ahmadu Haruna Zago, ya rasu bayan fama da rashin lafiya.

Ɗanzago ya kwashe shekaru da dama a harkar siyasa.

Ɗaya daga cikin ma’aikatan hukumar REMASAB ne ya tabbatar da rasuwar Ahmadu Haruna Zago a asibiti.

A ranar 5 ga watan Yulin shekarar 2023 Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya naɗa Haruna Zago a matsayin Shugaban Hukumar REMASAB.

Jama’a da dama na ci gaba da nuna alhinin rasuwar jigo a siyasar jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.

Related Post

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *